Sheikh Abdulkadir may Allah have mercy on him – was one of the greatest Islamic scholars and Imams of guidance. He was an important figure in the field of Theology Tauhid & jurisprudence in Bauchi city. He was one of those shining stars that
contributed to the learning and scholarship. He came from a family of scholars and led a life full of hard work and sacrifice for the sake of his religion, which his zeal for the realization of a good Muslim society that cherishes the true teachings of Islam as taught by our noble Prophet Muhammad (Sallallahu Alayhi wa Sallama) and understood by the early pious Muslim generations. A follower of Ash-arites and Malikates’ teaching, to this he gave his rather short life through disseminating the teachings of Islam by giving lessons, lectures, participating in seminars, issuing fatwas and other talks on various topics at different occasions.
Author: Shamjif
-

Biography Of Late Sheikh Abdulkadir Musa Jahun – Bauchi State
-

Gidauniyar Hidimmta Wa Dan-Adam: Aiyuka Na Raya Ilmi Da Gina Ƙasa Da Al’umma Mai Ɗorewa
Shaykh Abdulkadir Musa Jahun Islamic Foundation (SHAMJIF) Gidauniya ce ta sa kai wacce Marigayi Shaykh Abdulkadir Musa Jahun ya kafa da nufin yaɗa ilimin addinin musulunci musamman ilimin Alkur’ani, karatun Zaure (Ilmi), tarbiyyar ‘ya’yan Al’umma da tallafawa marayu da masu karamin karfi, wannan itace rayuwar sa kuma shine aikinsa har zuwa rasuwarsa.
JIHAR BAUCHI A TAƘAICE
Asalin Bauchi shine kalmar da ake amfani da ita ga daukacin yankin da ke kudu da kasar Hausa, amma daga baya sai aka gano shi da babban yankin da ke raba tafkin Chadi da tsarin kogin Neja-Benue. Tushen wannan babban dutsen ya ƙunshi wani babban fili na filayen ciyawa a tsayin ƙafafu 3,000-4,000 tare da kololuwar duwatsu masu tsayi zuwa ƙafa 7,000.
Bauchi jiha ce a arewacin Najeriya babban birninta shine babban garin Bauchi; tana da iyaka da jahohi bakwai bisa ga kididdiga ta ilmin jogirafi, jihohin sune:
Kano, Jigawa, Plateau, Kaduna, Adamawa, Taraba da Yobe.
An kafa jihar ne a ranar 3 ga Fabrairun 1976, kuma an kirkiro ta tare da Gongola (yanzu Adamawa), Niger, Benue, Ogun, Imo da kuma Ondo. Bauchi babban lardi ne da ya ƙunshi sassan Bauchi, Gombe (da farko) da Katagum wanda ya ƙunshi sassan mai kabilu da yaruka tare da albarkatun kasa.
Jihar Bauchi tana da kananan hukumomi 16 a baya, kuma a halin yanzu kamar yadda ta bunkasa tana da kananan hukumomi 20, wadannan su ne: Alkarei, Bauchi, Bogoro, Dambam, Darazo, Dass, Gamawa, Ganjuwa, Giade, Itas-Gadau, Jama’are, Katagum, Kirfi, Misau, Ningi, Shira, Tafawa Balewa, Toro, Warji da Zaki.
SHUGABANCI A JIHAR BAUCHI
Zamu iya kasafta shugabanci anan izuwa:
- Shugabanci na gwamnati
- Shugabanci na Sarauta
- Shugabanci na addini ( mai ɗauke da addinai biyu Musulunci da Kirista)
Shugabanci na gwamnati na gudana ne karkashin gwamna, anyi gwamnoni a Bauchi kamar haka:
- Mohammad Bello Khaliel March 1976 – July 1978 (Soja)
- Garba Duba July 1978 – October 1979 (Soja)
- Alh Abubakar Tatari Ali October 1979 – December 1983 (Siyasa jam’iyyar NPN)
- Mohammed Sani Sami January 1984 – August 1985 (Soja)
- Chris Abutu Garuba August 1985 – December 1987 ( Soja)
- Joshua Madak December 1987 – August 1990 (Soja)
- Abu Ali August 1990 – January 1992 (Soja)
- Dahiru Mohammed January 1992 – November 1993 (Siyasa, Jam’iyyar NRC)
- James Yana Kalau ( Kantomar) 9 December 1993 – 14 September 1994 (Soja)
- Rasheed Adisa Raji (Kantomar) 14 September 1994 – 22 August 1996 (Soja)
- Theophilus Bamigboye (Kantomar) 22 August 1996 – August 1998 (Soja)
- Abdul Mshelia (Kantomar) August 1998 – May 1999 (Soja)
- Ahmad Adamu Mu’azu 29 May 1999 – 29 May 2007 (Siyasa, Jam’iyyar PDP)
- Malam Isa Yuguda 29 May 2007 – 29 May 2015 ( Siyasa daga Jam’iyyar ANPP zuwa Jam’iyyar PDP) 27 June 2009
- M. A. Abubakar 29 May 2015 – 29 May 2019 (Siyasa Jam’iyyar APC)
- Sen.Bala Abdulkadir Mohammed 29 May 2019 (Siyasa, jam’iyyar PDP gwamna mai ci)
Shugabanci na Sarauta kuwa na gudana ne karkashin Sarakuna masu manyan masarauta wasu suna da tuta daga Shayhul Islami Shayhu Mujaddadi Usmanu Ɗanfoduye RaliyALLAHU sune akece dasu sarakunan yanka, sune:
- Mai Martaba Sarkin Bauchi Alh (Dr) Rilwanu Sulaimanu Adamu
- Mai Martaba Sarkin Katagum Alh Umar Faruk ll
- Mai Martaba Sarkin Misau Alh Ahmed Sulaiman
- Mai Martaba Sarkin Jama’are Alhaji Nuhu Ahmed Wabi
- Mai martaba sarkin Dass Alh. Uthman Bilyaminu Othman
Shugabanci na addini kuwa na hannun Zaƙakuran Malamai ne wanda suke da alaƙa da shugabanni kuma suna na mabiya gwargwadon dai ɓangarori da ake dasu cikin dukkan addinai.
TAKAITACCEN TARIHIN MALAM ABDULKADIR MUSA JAHUN
Malam AbdulKadir dan Musa (1938 – 2008) da rubuce-rubucensa.
Cikakken sunansa shi ne AbdulKadir dan Musa Jahun dan Hamid dan Aliyu dan Umar dan Abd’Allah. An haifeshi a wajejen shekarar 1938 a Unguwar Jahun a Bauchi. Iyayensa sun fito daga kabilar fulanin Jahun cikin jihar Kano ta wancan lokaci, yanzu kuma a jihar Jigawa. Ance Kakansa wani Malami ne mawadaci kuma yana daga cikin shahararrun Malaman Kano a zamanin Sarkin Kano Sulaiman daga bisani suka kaurato zuwa Bauchi a dalilin hidimar sarauta. Sune kuma ke rike da sarautar Galadiman Bauchi kafin ya faɗa hannu mai yi a yanzu, kanin Malam Abdulkadir Musa Jahun Alh. Ado Musa yayi sarautar Galadima. Shaykh Abdulkadir Musa Jahun ya taso a matsayin maraya, mai ladabi ga manya da malamansa, ya kwallafa ransa kan neman ilimi da sha’awar raya ƙasa da al’umma wanda har yau ana cin amfanin aiyukansa.
Malamansa:
Malam AbdulKadir dan Musa ya samu ilimin addinin musulunci da harshen larabci a matakin farko a wajen Kawunsa Malam Hamid (Limamin Jahun) wani malami mai saukin kai da fara’a. Ya kuma koyi ilimin addinin musulunci da harshen larabci mai zurfi daga marigayi Liman Mahmud dan Muhammad Babban Limamin Bauchi wanda ake kirgawa a cikin mashhuran malamai a Nigeria.
Bayan rasuwar Liman Mahmud, Malam AbdulKadir dan Musa ya cigaba da daukan karatu a wajen dan Liman Mahmud, Liman Ahmad dan Mahmud (Liman Baban Inna). Liman Ahmad dan Mahmud ya amince da Malam AbdulKadir dan Musa daga cikin dalibansa. Ya jawoshi a jikinsa sosai saboda zurfin fahimtarsa.
Wasu daga cikin Gudumawarsa:
Malam AbdulKadir dan Musa na daga cikin Shahararrun malaman zamaninsa a Masarautar Bauchi, ya bada wasu gudumawa ga addini da al’umma. Ya kafa makaranta mai suna Madrasah Ihya al-din Al-Islam. a shekarar 1979. Makarantar tana da sassa uku. su ne:
i. Sashen makarantar Allo
ii. Sashen makarantar Islamiyya don koyar da ilimin addini da larabci.
iii. Sashen Karatun Zaure don bada karatun littattafai ga manyan dalibai, inda akekara zurfafa sa ido kan dukkan harkokin koyarwa da koyon ilimi.
Ya kuma gina masallaci a harabar makarantar don gudanar da salloli biyar a kullum a shekarar 1980. Ya kuma assasa ginin masallatai da dama a ciki da wajen garin Bauchi. Wasu daga cikin ‘ya’yansa ne ke jagorantar Cibiyar, irin su Associate professor Dr. Muhammad Safiyyu AbdulKadir, Dr. Muhammad Mujtaba AbdulKadir, da Malam Muhammad Fadhilu AbdulKadir da sauransu.
RASUWARSA:
Malam AbdulKadir dan Musa wa kwanta jinya na kusan shekaru bakwai kuma yayi fama da shanyewar barin jiki wanda ya shafi wani sashen jikinsa. Kafin ya kwanta jinya, yakan ce lokacin mutuwarsa yayi kusa. Malam AbdulKadir dan Musa ya rasu a cikin daren 23 ga watan Maris na shekarar 2008 wanda yayi daidai da ran 16 ga watan Rabi’al Auwal na shekarar 1429, ran litinin aka bisneshi a gidansa dake Bauchi.
Rubuce-Rubucen Malam AbdulKadir dan Musa
1. Miftah al Tauhid: Wannan shi ne daya daga cikin manyan muhimman rubuce-“rubucen Malam AbdulKadir dan Musa. An rubuta shi da harshen larabci cikin wake kuma ya kunshi shafuka 15. A cikinsa ya soki littafin Sheikh Sanusi Gumbi mai suna “Wai shin Isa zai dawo? wanda ya rubuta cikin harshen hausa.
Malam AbdulKadir dan Musa bai kammala rubutunba kafin rasuwarsa. Yana da wasu littafan da ya rubuta da suka hada da:
2. Risalah an aqa’id al Tauhid, wa hiya auwal mabani al-Islam. Littafin ya fara da wasu fannoni na akidun Iman da Al-Islam a cikin shafuka.
3. Al-Ihsan: Wannan wani littafin ne rubutun hanu da aka samu a wajen Malam AbdulKadir dan Musa. Littafin ya kunshi shafuka hudu. Ya tattauna wasu bangarorin Al-Ihsan.
4. Risalah an Al Masjid: Littafi ne mai shafuka hudu dake cikakken bayanin ka’idojin Masallaci. Ya ambaci wasu ayoyin al-Qur’ani mai girma da Hadisan Manzon Allah suka shafi haka ciki har da wasu ka’idojin addu’a da Sunnah da ake aikatawa da suke da nasaba da Masallaci.
GIDAUNIYA
Gidauniyar tana aiki ne a matsayin duniyar tarbiyya da gina al’umma inda ta yaye dubban dalibai tun daga 1968-69 zuwa yau. Daga baya makarantar ta fadada tare da misalta matsayin Gidauniya mai yin hidima wa al’umma gwargwadon karfin ta. A yanzu an mata tsari mai ɗauke da sassa daban daban harda hukumar gudanarwa karkashin jagorancin shugabanta Mataimakin Farfesa Dr. Muhammad Safiyyu Abdulkadir, Aiyukan ta bai takaita kadai a karantar da mutane manya da yara ba kullum tana taɓo bangarori da dama na rayuwar al’umma.
Gidauniyar tana fikra kamar:
- Faɗaɗa binciken ilmin addinin Musulunci a zamanance
- Sauya fasalin zamantakewar al’umma da inganta dangantakarsu daidai da hauhawar zamani
- Gina kyawawan halaye a tsakanin yan ƙasa ta hanyar yi bita wa matasa
- Samar da ɗorewar tsaftar muhalli don samun tsaftataccen rayuwa. Da sauran su.
SASHIN MADRASA DA FALSAFARTA:
Makarantar Shaykh Abdulkadir (Madrasah) an kafa ta ne wuraren karshen 1960 wanda yanzu haka don haɓaka sassa daban daban na Gidauniyar ta yi rijista da hukumar CAC/IT/No. 146022, sannan kuma yayi rijista da gwamnatin jihar Bauchi a ma’aikatar matasa da wasanni karkashin lamba REG. MYS/B1/2001
A farko tana matsayin tsari a madadin zubin ilimi tsohon hanya mai shirin ɗaukar salo na zamani mai ƙarfi da tasari kamar zubin Halawiy na Sudan ko kuttab na Masar da makamantarsu. Mun ci gaba da kula da wannan tafarki tunda na bamu sakamakon ci gaba, haka ya kaimu muna ɗaukar sabbin shirye-shirye da yawa a hankali waɗanda ke tafiya da zamani ba tare da watsi da asali ba.
A yau muna ci gaba da al’adarmu a matsayin cibiyar share fagen karatu wanda ke iya riƙe dalibai a matakin makarantar kwana ba tare da yin Bara ba, kuma wasu tsare-tsare suna ƙara faruwa don inganta makarantar, a yanzu bisa alƙaluma muna da dalibai sama da 1000 a matakin shekarun dalibai 5-9 sai shekaru 9-15 da manya masu aji 25 zuwa sama a ayyukan koya da koyarwa daban-daban.
Muna ƙarfafa ɗalibai su yi aiki mai ɗorewa a rayuwarsu su zamo masu amfanar da iyaye da al’umma karkashin tsarin ilmantarwa kuma su ƙulla dangantaka ta addini da abokan zamantakewa na wasu addinai ko wasu kabilu don darajantawa.
Ana ƙarfafa kowane ɗalibi ya kasance mai tarbiyya da mutuntawa tare da fahimtar nauyin da ke kansa na al’ummarsa mai girma, yayin da tsarinmu na tsohon tsari da kuma wani bangare na zamani yana buɗe kofa da sanya kwazo wa yara suyi karatun zamani tare da koyon sana’o’i daidai da zamani da yanayi wanda ya hada da daidaitawa da koyar da kur’ani da wasu ilimin Larabci da Musulunci.
BAYANI:
Makarantar ta habaka zuwa Gidauniya mai suna Shaykh Abdulkadir Musa Jahun Islamic Foundation (SHAMJIF) a yau ta zamo gidauniya ce ta addini mai zaman kanta kuma tana da mabiya da dalibai daga wurare daban-daban a cikin kasar nan lura da yadda take karbar ɗalibai daga sassa daban daban musamman a Arewa, tana ba da ilimin addinin musulunci mai karfi da horarwa kyauta ( free Education), tare da ba da damar dalibai su ci gaba da karatun su na yau da kullum daidai da zamani.
Tsarin ilmantarwa na kullum shine ginshiƙin da ya samar da gidauniyar sai a yau ta zamo mai manufa, ƙima, wurin ba da ƙwakkwran ilimi, haɓaka ɗabi’a, da tarbiyya.
Gidauniyar tana bayar da tallafin karatu ga Almajiranta, marayun cikinta, da tallafawa marasa galihu don su samu wayewa na sanin muhimmancin neman ilmi ga maza da mata ta hanyar shigar da wasunsu makarantun firamare da sakandare na gwamnati, zuwa manyan makarantun islamiyya har zuwa matakin difloma da NCE.
MANUFOFI:
Gidauniyar ta na aiki ne don cimma manufofi kamar haka:
- Samar da tsara masu tsoron Allah da aiki don ci gaban al’umma
- Horar da dalibai kan ingantaccen Musulunci daidai da tsarin magabata ba zaƙewa ba noƙewa
- Kwadaitar da matasa son ci gaba a rayuwa tare da kula da dogaro da Kai cikin sana’o’i
- Sanya wa matasa son dabi’u na Musulunci don kare al’ummar musulmi daga fadawa cikin ta’addanci da tsattsauran ra’ayi.
- Aiki tare da nuna kyawawan halaye mai haɗa alaka da dangantaka tsakanin jagororin al’umma da shugabanninmu.
- Cusa wa masu tasowa sanin muhimmancin ƙasar mu da kiyaye ta barin rugujewa
DALIBAI:
Ɗaliban makarantar wannan Gidauniyar tana ɗauke da maza da mata wanda galibinsu yan Bauchi ne wasun kuma daga sauran wurare don karbar tarbiyyar addini.
A yanzu anata sabunta makarantar zuwa tsarin tafiya da zamani tare da kiyaye wasu tsofin al’adu musamman karatu da rubutu kan Allo.
Dalibai suna gudanar da ayyukansu na koyon ilmi da tarbiyya sau uku a kowace rana a cikin kwanaki biyar na mako, (asabar zuwa Laraba). Wasu daliban na karbar abinci ne kyauta, wasu kuwa ana ciyar da su karkashin kulawar iyayensu, wannan yana kare su daga fita neman abinci ko bara.
Tsofaffin ɗalibai suna taimakawa da aikin koyarwa da kula da dalibai ne kyauta a matsayin gudumowa wannan yana da alaƙa da horar da su da akayi lokacin suma suna cikin koyo. Wasu gyare-gyaren wuraren da ke ƙarƙashin odar shugabanni manyan ɗalibai ne ke yin su. Ana daukan Ɗalibai tare da yi musu rajista a kowane lokaci in iyaye na bukata.
ƁANGARORIN ILMI A GIDAUNIYA
Shaykh Abdulkadir Musa Jahun Islamic Foundation tana da sassan kamar haka:
- Sashen karatun Alkur’ani na Allo mai adadin almajirai fiye da ɗari tara (900)
- Sashen Hadda mai manufar kawo sauyi cikin yin Hadda a makarantun Allo daidai da zamani
- Bangaren Islamiyyah (wato koyon addini bayan ilmin Qur’ani)
- Sashen Zaure(Karatun Littafi) na Manya, wanda ke da tsari iri biyu:
- Darasi na daidaikun mutane a kwanaki 5 na mako
- Darasi na gama-gari/na jama’a a Masallacin bayan Magrib a ranakun Asabar da Litinin da Laraba kowane mako
5. Ajin koyon Larabci da karatun Islama na Manya
A ciki da wajen Bauchi dalibanmu na iya samun matsayi mai kyau na shaida a karatun Alkur’ani tare da Ibada da Ladabi da tarbiyyah
HIDIMAR RAYA ƘASA DAAL’UMMA:
Wani abu muhimmi shine Gidauniyar mu a duk sassanta tana ba da fifiko kan haɓaka kyawawan ɗabi’u, koyar da jagoranci, da hangen nesa don raya ƙasa. Waɗannan suna ba wa ɗalibai wasu tanade-tanade waɗanda za su iya taimakawa wurin aikin sa kai ako ina.
Ɗalibanmu suna samun dama daban-daban don haɓaka ƙwarewarsu a rayuwa a duk inda bukatar hakan ta taso.
Rukunin Manyan ɗalibai na hidima ga al’umma da kuma wayar da kan al’umma ta hanyar shirya laccoci don inganta tarbiyya, tsaron Kasa da Haƙurin zamantakewa na Addini ta hanyar gayyato ƙwararru daga waje da cikin gida. Najeriya.
Gidauniyar ta sha samun ziyarar baki daga wajen ƙasar mu Nigeria, inda akan shirya program da laccoci na horaswa na kwana 3 zuwa sati a wasu lokuta. Misali:
- Manyan Shehunan ilmi daga Jami’ar Azhar ta Masar a shekarar 2009 sindi
- Shayhun Malami Dr Abubakar Al Habshiy yazo daga Lebanon a shekarar 2018, ya dawo a 2019 da kuma 2020
- Mr Ayman yazo daga Syria a shekarar 2021
- Shaykh Dr Bilāl Al Hallāq yazo a karshen shekarar 2022 daga garin California ta ƙasar Amurka
- Wasu manya Ƙungiyoyin addini na gida Nigeria su kan ziyarce Gidauniyar lokaci lokaci.
Ayyukan sa kai:
Gidauniyar tana da wasu ayyukan al’umma na son raya ƙasa (Aikin sa Kai) da ta kanyisu ta hanyar haɗa wasu ɗalibai don yin ayyukan al’umma. Gidauniyar ta cim ma abubuwa masu zuwa kamar haka:
- Aikin tsaftar muhalli cikin unguwa
- Fita zuwa gyaran Makabarta
- Samar da akwatin agaji ta bada gudummawa musamman lokutan taron Maulidi
- Dashen bishiyoyi sau biyu a Bauchi Hajj Camp a watan Yuli ( July), 2021 da watan Mayu (May) na 2022
- Aikin hakar rijiyoyin burtsatse da rijiyoyi a lunguna da sako na cikin garin Bauchi kamar haka:
- Rijiyar burtsatse mai aiki da wutar lantarki a makarantarmu dake unguwar Jahun –Agusta 2017
- Rijiyar burtsatse mai aiki da wutar lantarki a Sabon Unguwar Dumi – 29/12/2022
- Rijiyar burtsatse mai aiki da wutar lantarki a Unguwar Gwallagan Cikin gari – 20/1/2023
- Rijiyar burtsatse a gundumar Miri – 30/1/2023
- Asalin rijiya (na tono) a Dumi – Nuwamba 2021
- Zauren Sulhu da kuma warware matsalolin al’umma
- Madaidaicin ɗakin karatu don amfanin Ɗaliban ilmi a dukkan matakai
- Shirya bita lokutan Azumi, lahiya, Hajji da dai wasu abinda ke bukatar ilmantarwa da tunatarwa.
- Samo gudummawa ta sayan abinci a raba wa al’umma musamman lokacin azumi da lokutan matsuwa kamar lokacin da aka yi covid 19
- Yanka shanu da raguna a raba wa masu karamin karfi da lahiya a ranar wadda ke zuwa ta hannun masu taimakawa
INGANTAWA:
Makarantar mu ta kasance makarantar Allo da Islamiyyah irin ta da (ta al’ada) yayin da lokaci ya chanja zuwa hauhawar zamani aka ci gaba, masu mallakar wurin sun inganta ta, ta yadda take kama da tsarin Tsangaya na gwamnati ta ke, hakan mun hanzarta ne wurin amsawa gwamnati kira da takeyi na sauyin yanayi da kalubale.
Ɗalibai na sa uniform duka da cewa makarantar Allo ce, ana yi wa ɗalibai rajista (ba tare da biyan kuɗi ba (ilimi kyauta), sai dai a sashin hadda kawai shi ana biyan dubu 3 duk zangon ( term) na karatu.
A halin yanzu dalibanmu suna samun horo da kula na zamani wanda ke ba su damar ci gaba da karatunsu don su iya shiga kwalejojin ilimi na fasaha da kimiyya har ma zuwa jami’o’i don nazarin abubuwan da suka dace na karatun Larabci da Islama da kuma abubuwan da ake bukata a cikin al’ummarmu na ilmin boko.
FATARMU:
Gidauniyar tana fata tare da addu’ar Allah ya sa gwamnati ta sa hannu don tallafawa wannan aiki na raya ƙasa, Muna fata wasu manyan kungiyoyi da cibiyoyi masu zaman kansu da ke bada tallafi ko kuma aiki da takeso ayi wa al’umma zata iya bamu muyi ko mu haɗa hannu ko kuma ta taimaka mana kai tsaye. Muna fata ALLAH ya huwace ko da daidaikun jama’a su tallafi irin wadannan gidauniyar kamar yadda itama ta ke taimakawa gwamnati da al’umma wajen baiwa ‘yan kasa ilimi da tarbiyya bisa gudumawa. Dangane da abubuwan more rayuwa kuwa muna cikin ƙanƙan da kai don neman kowane irin taimako ko tallafi daga amintattun kungiyoyi masu zaman kansu ko MDGs don samar mana da fili da gina sabon wuri ko faɗaɗa shi, ko ƙarin gyara don sake sabunta tsarin da muke da shi ta hanyoyin da suka dace. Wannan tabbas zai taimaka mana wajen aiwatar da haɓakarwa da samar da gyara cikin harkokin Almajiri/Tsangaya da tarbiyyan matasa. Gidauniyar ta na fatar
samar da ICT ko duk wani hanyar horar da matasa izuwa koyon sana’o’i don dogaro da Kai.